
Kamfanin dillancin labaran Iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin QAF cewa, an fara gudanar da wani shiri na bayar da horo kan kur’ani mai tsarki a birnin landan karkashin hubbaren Abbas (AS) tare da hadin gwiwa da makarantun kur’ani na kasar Birtaniya.
Bayanin ya ci gaba da cewa babbar manufar wannan shiri ita ce horar da malaman kur’ani mai tsarki a makarantun musulomi na kasar, domin sanin wasu daga cikin mas’aloli da ke bukatar Karin bayani da ilimi sosai.
Rahoton ya ce daga cikin muhimamn abubuwan da shirin zai mayar da hankalia kansu har da sanin ayoyi wadsanda aka shafe da kuam wadanda suka shafe su, gami sanin matsayin ayoyin hukunci da kuma masu bkatar Karin bayani.