
Kamfanin dillancin labaran iqna ya nakalto daga shafin sadarwa na Alriyad cewa, , Sheikh Muhammad Ayyub makarancin kur’ani mai tsarki kuma limami a masallacin manzon Allah (SAW) ya rasu yana da shekaru 68 da haihuwa.
Dan Sheikh Muhammad Ayyub ya bayar da labarin cewa mahaifin nasa ya rasu a shafinsa na yanar gizo na Twitter, kuma y ace za agudanar da janazarsa a makabartar Baki’a da ke Madina.
An haifi Mhammad Ayyub a cikin shekarar 1372 H a garin Makka kuma ya yi karatu a hannun Zaki Dagistani, da Sheikh Khalil, inda ya yi harda, daga nan kuma ya yi karatu a hannun Muhammad Abdulaziz Usaman, da Akram Diya Alumri, sai kuma Muhamamd Amin Shaqiti, da Abdulmuhsin Al-ibad.
Ya dais hara da sunan sheikh kurra, saboda kasantuwarsa yana bayar da salla da kuma karatun kur’ani a masallacin annabi.
Haka nan kuma ya yi sunan ta fuskar karatun kur’ani da kyautata sautinsa, inda yak an jagoranci sallar ashama ckin watan azumi, kuma ana saka karatnsa a cikin gidajen radio na kasar.