IQNA

Taro kan Dakunan karatun Kur’ani A Kasar Algeriya

20:50 - May 12, 2016
Lambar Labari: 3480405
Bangaren kasa da kasa, ana gudanar da wani zaman taron karawa juna sani kan muhimmancin dakunan karatun kur’ani a garin Shibli na lardin Balidah a kasar Algeriya.
Kamfanin dillancin labaran Iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo elbilad.net cewa, wannan taro na Alhoilaliya yana samn halaertar masana daga kasar ta Algeriya, da kuma wasu daga cikin kasashen musulmi da na larabawa.

Babbar manufar taron dai it ace yin dubi kan matsin dakunan karatun kur’ani da ake da su a kasashen musulmi na tarihi da suke bayar da gudunmawa ta fuskoki da dama.

Munir Talili daga jami’ar Zaituna ta kasar Tunisia, Muhammad Wuld Alda daga jami’ar Mauritania, Lui Isa jakadan Palastinu a kasar Algeriya, suna daga cikin wadanda suka gabatar da jawabi a wurin.

Masu bayanai sun ce a wurin, ya zama wajibi musulmi su mayar da hankali wajen karfafa lamurran kur’ani da kuma yadda za a kyautata su, musamman ta fuskar karatu da kuma warren karatun.

Kasar Algeriya dai na daga cikin kasashen da suka gina dakunan karatun kur’ani na gargajiya tun daruruwan shekarun da ska gabata, har zwa lokutan yaki tsakanin kasar da Faransa, a cikin shekara a 1954 zuwa 1962.

3496684

captcha