Kamfanion dillancin labaran iqna ya
habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na «Avvo.com» cewa, wasu mutane zaune gari
banza dauke da makamai sun kaddamar da harin a kan masallacin ne a lokacin da
ake gudanar da salla a cikinsa a birnin na Lagos.
Majiyoyin ‘yan sanda a birnin sun bayyana cewa, mutanen da suka kaddamar da wannan harin sun kafa wata kungiya ta yan daba da ta sabawa kaida da doka, wanda hakan yasa a ka kame su, amma an sake bayan da aka karbi belin nasu.
Bayan fitowarsu sun fara da kai hari kan masallaci a lokacin mutane suke salla, duk kuwa da cewa babu wanda ya rasa ransa ko jikkata, amma sun bata bangayen masallacin.