Kamfanin dillancin labaran iqna ya
habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gioz na dakar.icro
cewa, Sheikhuna Lauh shugaban darikar muridiyyah a kasar Senegal ya gana
da karamin jakadan Iran a kasar Sayyid Hassan Heshmatim, inda ya tabbatar masa
da fara gudanar da wannan aiki.
Sheikhuna Lauh y ace hakika ya ji dadin yadda ya kasance mai tarjama kalmomin Imam Ali (AS) daga littafin Nahjul Balagha, kasantuwar hakan babban abin alfahari gare shi, kuma hakan yana zaman Karin haske ne gare shi.
Sheikhuna Lauh ya kasance daya daga cikin bakin da aka gayyata zuwa gasar karatun kur’ani ta duniya a birnin Tehran a matsayin daya daga cikin baki na musamman.
Ya tarjama kur’ani mai tsarkia cikin harshen Wolof wanda kasar Libya ta dauki nauyin buga su tare da raba a masallatai da ke kasashen Afirka.