IQNA

An Sanar Da Sunayen Wadanda Suka Nuna Kwazo A Gasar Nakasassu A Iran

23:52 - May 16, 2016
Lambar Labari: 3480418
Bangaren kas ada kasa, an sanar da sunayen wadanda suka nuna kwazoa gasar kur’ani ta nakasassu ta duniya da ake gudanarwa a Iran.
Kamfanin dillancin labaran Iqn aya habarta cewa, a daidai lokacin da ake gudanar da gasar kur’ani ta dniya karo na talatin da uku, ana kuma gudanar da gasar masu nakasa ta kasa da kasa.

Ita dai wannan gasa ana gudanar da ita ne a babban masallacin marigayi Imam kamar dai yadda ake gudanar da gudar gasar a nan.

Abdulgafur Jauharchi daga kasar Iran shi ne ya zo na daya, sai kuma Ahmat Sarikaya daga Turkiya da kuma Sabirin Muhammad Zu’aibi daga kasar Tunisia, su ne suka na biyu da kuma na uku.

Wannan gasa tana gudana ne a babban masallacin marigayi Imam Khomenei (RA) da ke birnin Tehran, tare da halartar dukkanin wakilan da suka wakilci kasashensu.

A gobe ne dai ake kamala wannan gasa, inda za a bayar da kyautuka ga wadanda suka nuna kwazo, da ma saran dukkanin wadanda suka halrci gasar.

3498382

captcha