IQNA

Desh Ta Dauki Alhakin Harin Syria

22:03 - May 23, 2016
Lambar Labari: 3480442
Bangaren kasa da kasa, kngiyar Daesh ta dauki alhakin harin ta’addanci a kan biranan Tartus da Jabla na kasar Syria.

Kamfanin dillancin labaran Iqna ya nakalto daga shafin press TV cewa an tayar da wasu jerin bama bamai a cikin mota sannan kuma an kai hare-haren kunar bakin-wake a birane biyu da ke gabar teku a yankin Latakia da ke hannun gwamnatin Syria.

Masu fafutuka sun bayyana cewa mutum fiye da 100 sun mutu bayan fashewar wasu abubuwa kusa da tasoshin motocin safa a Tartous da kuma Jableh wadanda a baya ba sa cikin jerin wuraren da ake rikici.

An kuma bayar da rahoton cewa an kai wani hari a wani asibiti a Jableh.

Wata kafar yada labarai ta kungiyar mayakan IS ta yi ikirarin kai hare-haren.

Rasha, wacce take marawa Shugaban kasar baya, na da sansanin sojin ruwa a Tartous, yayin da sansaninta na sama ke kusa da Jableh.

Wani kakakin gwamnatin Rasha, ya ce hare-haren na nuni da bukatar ci gaba da tattaunawar zaman lafiya a Syria.

Rasha ta fara kaddamar da hari kan sansanonin yan ta’adda a cikin kasar Syria tare da izinin gwamnatin kasar, wanda hakan ya karya lagon yan ta’adda matuka, kuma shi ne babban dalilin da ya sanya suke daukar matakan kai harin bam a halin yanzu a cikin wadannan yankuna.

3500413

captcha