
Kamfanin dillancin labaran Iqna ya nakalto daga shafin press TV cewa an tayar da wasu jerin bama bamai a cikin mota sannan kuma an kai hare-haren kunar bakin-wake a birane biyu da ke gabar teku a yankin Latakia da ke hannun gwamnatin Syria.
Masu fafutuka sun bayyana cewa mutum fiye da 100 sun mutu bayan fashewar wasu abubuwa kusa da tasoshin motocin safa a Tartous da kuma Jableh wadanda a baya ba sa cikin jerin wuraren da ake rikici.
An kuma bayar da rahoton cewa an kai wani hari a wani asibiti a Jableh.
Wata kafar yada labarai ta kungiyar mayakan IS ta yi ikirarin kai hare-haren.
Rasha, wacce take marawa Shugaban kasar baya, na da sansanin sojin ruwa a Tartous, yayin da sansaninta na sama ke kusa da Jableh.
Wani kakakin gwamnatin Rasha, ya ce hare-haren na nuni da bukatar ci gaba da tattaunawar zaman lafiya a Syria.
Rasha ta fara kaddamar da hari kan sansanonin yan ta’adda a cikin kasar Syria tare da izinin gwamnatin kasar, wanda hakan ya karya lagon yan ta’adda matuka, kuma shi ne babban dalilin da ya sanya suke daukar matakan kai harin bam a halin yanzu a cikin wadannan yankuna.