IQNA

Mabiya Addinin Buda Na Keta Alfarmar Masallatan Musulmi A Myanmar

21:55 - June 27, 2016
Lambar Labari: 3480559
Bangaren kasa da kasa, Masu tsattsauran ra'ayi na mabiya addinin Buda a kasar Myanmar suna ci gaba da cin zarafin musulmi da keta alfamar masallatai da wuraren ibada na mabiya addinin muslunci.
Kamfanin dilalncin labaran kur'ani na Iqna ya habarta cewa, Tashar talabijin ta alalam ta bayar da rahoton cewa, a cikin 'yan kwanakin nan 'yan buda masu tsattsauran ra'ayi sun ci zarafin musulmi a wurare da dama a cikin kasar Myanmar, kuma hakan yana faruwa ne tare da cikakken goyon bayan gwamnatin kasar, tare da yin rufa-rufa wajen hada labarin hakan ya watsu a duniya.

Rahoton ya ce baya ga hain da 'yan buda suka kai a daren Juma'ar da ta gabata a garin Bago, inda suka rusa babban masallacin musulmi tare da banka masa wuta, sun kai hare-hare a wasu sassa na kasar a kan musulmi, inda suka keta kwafi-kwafi na kur'ani mai tsarki, amma kafofin yada labaran kasar suna boye labarin.

Kungiyoyin kare hakkin bil adama na kasa wadanda suka hada har da Amnesty Int. a cikin wannan makon sun bukaci da a gudanar da binciken gaggawa kan abin da yake faruwa na cin zarafin musulmi a kasar Myanmar, tare da daukar matakai na kare rayukansu da dukiyoyinsu, da kuma gurfanar da duk wanda aka samu da hannun wajen muzgunawa musulmi a gaban kuliya.

3510704

captcha