Kamfanin dilalncin labaran Iqna
ya habarta cewa, ya nakalto daga jaridar Indepent cewa, sakamakon bincike kan
lamurra da suka danganci ta'addanci jami'an tsaro sun tsananata bincike a cibiyoyin
muslunci a Totengham da Liton.
Bayanin ya ci gaba da cewa an dauki wannan matakin ne bayan da aka ga ana ajiye wasu ledoji da aka kunshe da ba a san abin da ke ciki ba.
Hakan kuwa sakamako ne na nuna kyamar musulmi da wasu ke yi a kasar da kuma nuna alamu na cutar da su, wanda hakan ya saka shakkua cikin zukatan musulmi kan manufar hakan.
Sai daga bisani bayan gudanar da bincike kan wasu daga cikin irin wannan kunshi da aka samu ana ajyewa a wasu cibiyoyin musulmi an samu wata hoda wadda ba za ta iya cutar da dan adam ba.
A cikin shekarar da ta gabata an samu cutar da musulmi har sau 326 a fadin kasar, wanda hakan ne nuni da cewa kyamar musulmi na ci gaba da karuwa a kasar fiye da kowane lokaci.
Wannan lamari dai ya fi shafar mata muulmi wadanda suke aka hijabi, wadanda ake saurin gane su daga shigarsu da kuma tufafin da suek sakawa.