Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin
hulda da jama'a na cibiyar yada al'adun musunci cewa, an gudanar da zaman taron
bayar da horon wanda shi ne irinsa na farko a cikin nasara, tare da halartar
malaman kur'ani 23 daga larduna 14 na kasar ta Senegal a ginin cibiyar ta
jami'ar Almustafa (S).
An dai koyar da abubuwa da dama da suka danganci kur'ani kama da kira'a da salo daban-daban, da kuma kayutata tajwidi da wasu hukunce-hukunce na karatu.
Sayyid Hassan Esmati shugaban ofishin kula da harkokin al'adu na kasar Iran a kasar ta Senegal da kuma Sheikh Mustafa Lu, daya daga cikin manyan malaman addini na kasar duk sun halarci wurin rufe wannan taro na bayar da horo.
Masana da malamai na kasar ta Senegal da suka halarci wurin sun yaba matuka da yadda kasar Iran tak ebayar da muhimmanci wajen yada ilmomin kur'ani mai tsarki a kasar tare da halartar makaranta daga kasar a wannan taro.