A fili take kan cewa duk wadanda suka aikata wannan aika-aika sun yi hakan ne da nufin harzuka musulmi, domin kuwa dukkanin musulmi ba za su ji dadin abin da ak ayi na keta alfarmar masallatai ba.
Baya da keta alfarmar masallatai wadanda wuraren ibada na musulmi, an kuma keta alfarmar kur’ani mai tsarki.
Har yanzu dai ba iya tantance mutanen da suka aikata wannan abu ba, amma dai jami’an tsaro sun ce sun shiga gudanar da bincike kan lamarin, domin gano dukkanin wadanda suka aikata hakan tare da gurfanar da sua gaban kuliya, domin fuskantar sakamakon aikinsu.