Bayanin ya ci gaba da cewa a yayin ganawar tasu sun tattauna muhimamncin da ke tattare da neman ilimi, wanda kuma kuma ko shakka babu wasu da dama daga mutanen Najeriya suna da shawar su je su karatu na addini a kasar ta Iraki, a kan haka aka bayar da guraben karatu ga mutane goma sha daya daga cikin mabiya harkar musulunci.
Hka nan kuma a nasu bangaren malamai da dama akasar ta Iraki sun nuna farin cikinsu danagne da yadda yan Najeriya da dama suka samun damar zuwa tattakin arbaeen na Imam Hussain a wannan shekara da wasu shekaru da suka gabata.
Kamar yadda suka yi fatan ganin mahukuntan Najeriya sun saki jagoran harkar muslunci da suke tsare da shi a halin yanzu domin samun damar yi masa magani.
Su ma a nasu mabiya harkar musulunci yi godiya matuka dangane da irin karamcin da aka nuna msuu a wannan trao mai albarka daga bangaren al’ummar kasar Iraki.