IQNA

An Gudanar Da Zaman Sirri Tsakanin Isra'ila Da Wasu Larabawa A Masar

21:05 - June 29, 2017
Lambar Labari: 3481654
Bangaren kasa da kasa, jaridar Ra'ayul Yaum ta nakalto daga wata majiyar diplomasiyya ta larabawa da ke tabbatar da cewa an gudanar da zama a tsakanin Isra'ila da wasu larabawa a kasar masar.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya bayar da rahoton cewa, jaridar wadda take mayar da hankali wajen bayar da labaranta dangane da siyasar kasashen larabawa da yankin gabas ta tsakiya, ta habarta cewa, majiyoyin diplimasiyyar sun tabbatar mata da cewa an gudanar da zaman ne a birnin Alkahira fadar mulkin kasar Masar a makon da ya gabata.

Jaridar ta kara da cewa, an gudanar da wannan zaman a sirri ne a tsakanin wakilan Isra'ila, Saudiyya, Amurka, UAE, Masar da kuma Jordan, kuma zaman yana da dangantaka ne da batun yankin Palastinawa na zirin Gaza, da ke karkashin ikon kungiyar Hamas, wadda sukkanin kasashen da suka halarci zaman suke kallonta a matsayin kungiyar ta'adanci.

Zaman ya gudana ne a cikin sirri matuka, a kan haka babu cikakken bayani kan abubuwan da aka tattauna dalla-dalla, amma bisa ga dukkanin alamu akwai wani boyayyen lamari da ake kitsawa a kan yankin na Gaza, da Isra'ila take ci gab ada killace shi tsawon shekaru.

3613839

 

Abubuwan Da Ya Shafa: iqna kamfanin dillancin labaran iqna
captcha