Jaridar ta kara da cewa, an gudanar da wannan zaman a sirri ne a tsakanin wakilan Isra'ila, Saudiyya, Amurka, UAE, Masar da kuma Jordan, kuma zaman yana da dangantaka ne da batun yankin Palastinawa na zirin Gaza, da ke karkashin ikon kungiyar Hamas, wadda sukkanin kasashen da suka halarci zaman suke kallonta a matsayin kungiyar ta'adanci.
Zaman ya gudana ne a cikin sirri matuka, a kan haka babu cikakken bayani kan abubuwan da aka tattauna dalla-dalla, amma bisa ga dukkanin alamu akwai wani boyayyen lamari da ake kitsawa a kan yankin na Gaza, da Isra'ila take ci gab ada killace shi tsawon shekaru.