Bangaren kasa da kasa, Kotun soji a kasar Masar ta yanke hukuncin daurin rai da rai a kan wasu magoya bayan kungiyar Muslim Brotherhood su 58, bisa zarginsu da kai hari a kan wuraren tsaro a lokacin da aka hambarar da Muhammad Morsi.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta
cewa, tashar talabijin ta al'alam ta bayar da rahoton cewa, a zaman da kotun
sojin ta gudanar ta bayyana cewa, dukkanin mutanen 58 suna da hannu a harin da
aka kaddamar kan ofishin 'yan sanda da ke garin Asyut, a lokacin da ake gudanar
da zanga-zangar da ta kai ga hambarar da Muhammad Morsi daga kan shugabancin
kasar a 2013.
Kotun ta ce dukkanin mutanen 58 da ake tuhuma mambobi ne na
kungiyar muslim Brotherhood, kuma ta yanke hukuncin daurin rai da rai a kansu.
Shugaban kasar mai ci a yanzu Abdulfattah Sisi ya yi amfani
da damar da ya samu a lokacin da mutane suke yin zanga-zangar nuna adawa ga
Muhammad Morsi, inda kasashen Saudiyya da hadaddiyar daular larabawa suka
taimaka masa wajen hambarar da shi, inda ya dare kan shugabancin kasar har zuwa
yanzu.
3623781