IQNA

22:58 - November 23, 2017
Lambar Labari: 3482130

Cibiyar Azhar Ta Yi Allah wadai Da Harin Ta’addanci A Najeriya

Bangaren kasa da kasa, cibiyar Azhar da ke kasar Masar ta fitar da bayanin yin tir da Allah wadai da harin ta’addancin da aka kai a Mubi da ke jahar Adamawa.

Cibiyar Azhar Ta Yi Allah wadai Da Harin Ta’addanci A Najeriya

Kamfanin dillancin abaran iqna ya habarta cewa, cibiyar Azhar da ke kasar Masar ta fitar da bayanin yin tir da Allah wadai da harin ta’addancin da aka kai a Mubi da ke jahar Adamawa wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane fiye da hamsin.

Azhar a cikin bayanin ta bayyana cewa, wannan abin da ya faru a Najeriya yana daga cikin sakamako na yaduwar akidar ta’addanci da sunan adini, wanda hakan ya yi hannun riga da hakikanin koyarwar addinin muslunci.

Haka nan kuma bayanin ya kira a kan wajabcin yaki da ta’addanci tun daga asasi, domin kuwa da karfi ba za a iya kawar da ta’addanci ba domin kuwa akida ce wadda wahabiyanci ne tushenta, amma ta hanyar yaki da wannan akida a ilmance da kuma hanyoyi na fadakarwa, za a samu nasara wajen rage kaifin lamarin.

Ita ma a nata bangaren kungiyar kasashen musulmi ta yi tir da Allah wadai da wannan aiki na ta’addanci, inda aka kai hari kan masalata da suke sallar asubahi a garin Mubi na jahar Adamawa, inda mutae fiye da 5 suka sara rayukansu, wasu kuma suka jikkata.

3665851


captcha