Bayanin ya ci gaba da cewa an gabatar da littafai kimanin 67 da aka rubuta acikin harsunan faransanci da kuma larabaci da aka rubuta a Iran da Senegal.
Babbar manufar wanann baje koli dai ita ce bayyana matsayin dukkanin bangarorin biyu na malaman Iran da kuma na Senegal, wadanda dukkaninsu sun hadua kan abubuwa da dama, musamman soyayya ga ahlul bait.
Za a kammala wannan baje koli ne gobe, tare da gabatar da jawabai ga maharta wurin, inda za a bayyana mahangar malaman biyu Imam Khomeni (RA) da kuam sheikh Amadu Bamba a kan lamurra da suka shafi tafsirin wasu surori na kur'ani.