IQNA

Baje Kolin Littafan Malaman Iran da Senegal A Dakar

23:19 - November 25, 2017
Lambar Labari: 3482137
Bangaren kasa da kasa, an bude wani baje koli a birnin Dakar na kasar Senegal na littafai da aka rubuta kan manyan malaman Iran da Senegal da suka hada da Imam Khomenei (RA) da kuam Sheikh Amadu Bamba.
Baje Kolin Littafan Malaman Iran da Senegal A DakarKamfanin dillancin labaran iqn aya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na cibiyar yada al'adun musulunci cewa, a jiya an bude wani baje koli a birnin Dakar na kasar Senegal na littafai da aka rubuta kan manyan malaman Iran da Senegal da suka hada da Imam Khomenei (RA) da kuam Sheikh Amadu Bamba jagoran darikar Muridiyya a kasar.

Bayanin ya ci gaba da cewa an gabatar da littafai kimanin 67 da aka rubuta acikin harsunan faransanci da kuma larabaci da aka rubuta a Iran da Senegal.

Babbar manufar wanann baje koli dai ita ce bayyana matsayin dukkanin bangarorin biyu na malaman Iran da kuma na Senegal, wadanda dukkaninsu sun hadua kan abubuwa da dama, musamman soyayya ga ahlul bait.

Za a kammala wannan baje koli ne gobe, tare da gabatar da jawabai ga maharta wurin, inda za a bayyana mahangar malaman biyu Imam Khomeni (RA) da kuam sheikh Amadu Bamba a kan lamurra da suka shafi tafsirin wasu surori na kur'ani.

3666582


captcha