IQNA

23:31 - July 09, 2018
Lambar Labari: 3482818

Wasu ‘Yan Majalisar Isra’ila Sun Shiga Masallacin Quds

Bangaren kasa da kasa, wasu daga cikin ‘yan majalisar haramtacciyar kasar Isra’ila sun kutsa kai a cikin masallacin quds mai alfarma.

Wasu ‘Yan Majalisar Isra’ila Sun Shiga Masallacin Quds

 

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, wasu daga cikin ‘yan  majalisar haramtacciyar kasar Isra’ila sun kutsa kai a cikin masallacin quds mai alfarma da nufin keta alfarmar wannan wuri mai albarka.

Yahudawan sun shiga cikin masallacin ne tare da kariya daga daruruwan jami’an tsaron Isra’ila.

A cikin ‘yan kawanakin nan dai yahudawa suna yawan shiga cikin wannan masallaci mai alfarma domin tsonakar al’ummar musulmi.

Tun bayan da shugaban Amurka ya ayyana birnin Quds a matsayin babban birnin yahudawan Israila a hukumance, yahudawan suke ta kara cin karensu babau babbaka  a kan musulmi da wurare masu tsarki a wannan birni.

3728765

 

captcha