IQNA

23:41 - August 25, 2018
Lambar Labari: 3482924

Masallacin ‘Yan Shia Za Dauki Nauyin Taron Ghadir A Kenya

Bangaren kasa da kasa, masallacin mabiya mazhabar shi’a a kasar Kenya zai dauki nauyin taron idin Ghadir.

Masallacin ‘Yan Shia Za Dauki Nauyin Taron Ghadir A Kenya

 

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, shafin yada labarai na ciyar yada al’adun musulunci ya bayar da rahoton cewa, masallacin mabiya mazhabar shi’a a kasar Kenya zai dauki nauyin taron idin Ghadir khom da za a gudanar a mako mai zuwa.

Wannan taro dai zai samu halartar malamai da kuma masana daga bangarori daban-daban, daga ciki kuwa akwai wadanda za su gabatar da jawabi da kuma kasidu kan matsayin wannan rana, da kuma darussan da ke cikinta.

Bayan nan kuma za a gabatar da sallolin azuhura da la’asar a wurin kafin ci gaba da taron.

 

3741075

 

 

captcha