IQNA

Yahudawa Sun Keta Alfarmar Masallacin Quds

23:58 - September 27, 2018
Lambar Labari: 3483017
Bangaren kasa da kasa, Majiyar Palasdinawa ta ce; 'Yan share wuri zauna 159 ne su ka kutsa cikin masallacin kudus a karkashin kariyar sojojin sahayoniya

 

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, Kutse cikin masallacin kudus ya fara zama jiki inda a kowane mako 'yanhudawa 'yan share wuri zaune su ke shiga cikinsa sau daya ko sau biyu.

a gefe daya sojojin sahayoniya sun kai hari a yankuna daban-daban na yammacin kogin Jordan, inda su ka yi awon gaba da palasdinawa sha biyar ba tare da tuhumarsu da wani laifi ba.

Bayan kamun mutane, an yi taho mu gama a tsakanin samarin palasdinawa da kuma sojojin 'yan sahayoniya.

Da a kwai Palasdinawa dubu shida da dari biyar a cikin kurkukun haramtacciyar kasar Isra'ila, dari uku daga cikinsu kananan yara.

 

3750694

 

 

 

captcha