Sadiqul-Mahdi ya kuma kirayi magoya bayansa da su shiga cikin masu Zanga-zangar ruwan sanyi ta yin kira ga shugaba Umar Hassan al-Bashir da ya sauka daga kan mukaminsa
Bugu da kari shugaban na Jam'iyyar Ummah ya yi kira da a saki dukkanin fursunonin siyasa, sannan kuma ya bayyana cewa ya zuwa yanzu an kashe mutanen da su ka kai 50
Tun ranar 19 ga watan Disamba na shekarar da ta gabata ne al'ummar kasar Sudan su ka fara yin Zanga-zangar kin yarda da hauhawar farashin kayan masarufi. Sai da daga baya Zanga-zagar ta juye zuwa yin kira ga shugaban kasa Umar Hassan al-Bashir da ya yi murabus
Majiyar gwamnati ta ce adadin mutane da aka kashe a tsawon lokacin Zanga-zangar ba su wuce 29 ba, yayin da kungiyoyin kare hakkin bil'adama suke cewa an kashe mutane 40.
Wannan ce bijirewa mafi girma da mutanen kasar ta Sudan suke yi a tsawon shekarun mulkin Shugaba Umar Hassan al-Bashir wanda ya fara tun a 1993.