IQNA

An Kai Wa Wasu mata Biyu Musulmi Hari A Kasar Faransa

22:17 - October 21, 2020
Lambar Labari: 3485294
Tehran (IQNA) an kai wa wasu mata biyu musulmi haria  kasar faransa tare da daba musu wuka.

Tashar alalam ta bayar da rahoton cewa, a yau an kai wa wasu mata biyu musulmi da suke sanye ad lullubi hari da wukake a cikin birnin Paris fadar mulkin kasar faramsa.

Cibiyar da ke sanya ido kan kare hakkokin musulmia  nahaiyr turai ta bayyana wannan harin da cewa na ta’addanci ne, kuma daidai yake da duk wani hari da ake kira na ta’addanci ba tare da laakari da wane ne ya kaddamar da harin ba.

Wannan cibiya ta bayyana cewa, kin jinin musulmi a kasar faransa ya karu matuka, wanda kuma ba daidai ba ne a dora karan tsana  akan dukkanin musulmi a kasar, domin kuwa abin da ake fakewa da shi na ayyukan masu tsatsauran ra’ayi daga cikin musulmi, ko musulmi ba su tsira ba.

A kan haka bayanin y ace dole mahukunta  akasar ta faransa su dauki matakai na ganin sun kare musulmi kamar yadda ake kare kowane dan kasa, domin su ma ‘yan kasa da suke da ahkkoki kamar kowa, kuma dole ne a kare musu hakkokinsu kamar yadda kundin tsarin mulkin kasar ya tanada.

 

3930680

 

 

captcha