IQNA

23:13 - May 13, 2021
Lambar Labari: 3485910

Ayatollah Sistani: Dole Ne Musulmi Su Taimaka Ma Al'ummar Falastinu

Tehran (IQNA) babban malamin addini na kasar Iraki Ayatollah Sayyid Ali Sistani ya yi kira zuwa ga taimakon al’ummar Falastinu marasa kariya.

Ayatollah Sistani: Dole Ne Musulmi Su Taimaka Ma Al'ummar Falastinu

A cikin bayanin da ofishin babban malamin addini na kasar Iraki Ayatollah Sayyid Ali Sistani ya fitar a jiya, shehin malamin ya yi kira ga dukkanin musulmi da ma sauran al’ummomin duniya masu lamiri, da su taimaka ma al’ummar Falastinu, wajen taka wa Isra’ila burki a kan kisan kiyashin da take yi musu.

Bayanin Ayatollah Sistani ya yi ishara da irin mawuyacin halin da gwamnatin yahudawan Isar’aila ta jefa al’ummar Falastinu a ciki tsawon shekaru fiye da saba’in, wanda kuma har yanzu Falastinawa suna cikin wannan mawuyacin hali.

A cikin bayanin nasa, Ayatollah Sistani ya yi Allawadai da kakkausar murya dangane da hare-haren da Isra’ila take kaddamarwa akan al’ummar Falastinu a halin yanzu, a zirin Gaza da birnin Quds da sauran yankunan Falastinawa.

Ya yi ishara da keta alfarmar wurare masu tsarki da Isra’ila take yi musamman a cikin watan Ramadan mai alfarma, da hakan ya hada da masallacin Quds alkiblar musulmi ta farko, mafi muni kan hakan kuma shi ne shekar da jinin muuslmi a cikin wanann wuri mai alfarma a cikin watan watan Ramadan.

Daga karshe Ayatollah Sistani ya yi kira ga sauran bangarori na kasa da kasa da su sauke nauyin da ya rataya a kansu dangane da halin da ake ciki a Falastinu.

 

 

 

3971332

 

 

 

 

captcha