
Shugaban kasar Iran Ibrahim Ra'isi ya bayyana cewa gazawar Amurka a kasar Afghanistan, wata dama ce ta wanzar da zaman lafiya a Afghanistan.
A martanin farko da ya mayar bayan da ‘yan Taliban suka kwace iko da Kabul, shugaba Ra’isi, ya ce ya kamata ficewar sojojin Amurka, ya zama wata dama ta tabbatar da zaman lafiya da tsaro a Aghanistan.
Ya kuma yi kira ga dukkan bangarorin Afghanistan dasu cimma matsaya ta siyasa domin jagorancin kasar.
Iran, ta kuma ce a shirye ta ke ta taimaka wajen dawo da zaman lafiya a makobciyar kasar Afghanistan.
Dama dai Iran ta jima da take kalubalantar kasancewar sojojin Amurka a kasar ta Afghanistan dama yankin baki daya.
Iran dai na kallon kasancewar Amurka a yankin a matsayin barazana ga zaman lafiya da tsaro.