IQNA

Jagoran Juyi Na Iran Ya Yabawa Kokarin Da 'Yan Wasan Kasar Suka Yi A Gasar Motsa Jiki Ta Nakasassu

18:40 - September 05, 2021
Lambar Labari: 3486273
Tehran (IQNA) jagoran juyin juya halin muslucni na Iran ya jinjina wa 'yan wasan kasar kan nuna kwazon da suka yia gasar motsa jiki ta nakasassu.

Kamfanin dilalncin labaran iqna ya bayar da rahoton cewa, jagoran juyin juya halin muslunci na Iran Ayatollah Sayyid Ali Khamenei ya jinjina wa 'yan wasan kasar kan nuna kwazon da suka yi a gasar motsa jiki ta nakasassu ta duniya.

Ga matanin sakon:

Da sunan Allah mai rahama mai jin kai

Ina godiya matuka da kuma yin jinjina ga 'yan wasan Iran da suka nuna kwazo a a gasar motsa jiki ta nakasassu ta duniya wadanda suka faranta ran 'yan kasarsu ta hanyar samun lambobin yabo na zinariya.

Sayyid Ali Khamenei 

4 Satumba 2021

 

 

3995109

 

captcha