IQNA

Ana Bukin Cikar Shekaru 67 Da Kafa Dakarun Gwagwarmayar Kwatar ‘Yancin Kai A Aljeriya

19:50 - November 01, 2021
Lambar Labari: 3486499
Tehran (IQNA) a yau ne ake gudanar da bukin cikar shekaru 67 da kafa kungiyar dakarun kwatar ‘yancin kan kasar Aljeriya daga ‘yan mulkin mallaka.

A kasar Aljeriya a yau ne ake gudanar da bukin cikar shekaru 67 da kafa kungiyar dakarun kwatar ‘yancin kan kasar daga ‘yan mulkin mallakar kasar Faransa.

Shekaru 67 da suka gabata a rana irin ta yau wato  1 Nuwamban1954 Aka kafa dakarun kwatar 'yancin kan kasar Aljeriya karkashin jagorancin Ahmad Bin Billa, da haka kuma aka fara gwagwarmayar neman samun 'yencin kai na kasar Algeriya.

Tun a farkon karni na 19 miladiyya ne sojojin kasar Faransa suka mamaye kasar Algeria, sannan dukkanin yunkurin da mutanen kasar suka yi ta yi  a tsawon shekaru 132 ya ci tura.

Amma daga karshe turawan sun  bawa kasar yancin kai a shekara 1962.

Sannan Ahmad Bin Billah ya zama shugaban kasar Algeriya na farko bayan samun 'yencin kai.  Sai kuma a shekara ta 1965 aka yi masa  juyin mulki.

Ana daukar Ranar kafa dakarun kwatar 'yancin kasar Algeriya, a matsayin kasa a hukumance.

برپایی موزه سیار در الجزایر به منظور روایت تاریخچه انقلاب علیه استعمار فرانسه

برپایی موزه سیار در الجزایر به منظور روایت تاریخچه انقلاب علیه استعمار فرانسه

برپایی موزه سیار در الجزایر به منظور روایت تاریخچه انقلاب علیه استعمار فرانسه

 

 

4009541

 

Abubuwan Da Ya Shafa: kafa dakaru
captcha