IQNA

Shugaban Afirka Ta Kudu Ya Yi Gargadi Dangane Da Barazanar Daesh

16:09 - November 24, 2021
Lambar Labari: 3486600
Tehran (IQNA) Cyril Ramafoza ya ce kungiyoyi irin su ISIS da suka kai hari a kasashen Afirka irin su Mozambik da Uganda, za su iya isa Afirka ta Kudu.

Jaridar Daily Maverick ta bayar da rahoton cewa, Shugaban na Afirka ta Kudu ya yi gargadin ne a wani taron manema labarai na hadin gwiwa da takwaransa na Kenya, Uhoru Kenyatta, game da barazanar kungiyar ISIS da makamantansu a Afirka ta Kudu, yana mai cewa ba za a taba yin watsi da barazanar tayar da kayar baya ba, sannan a mai da hankali kan kasa guda dunkulalliya.

Ramaphosa ya ce, Wadannan kungiyoyi da suka zo da sunaye daban-daban suna da hadin gwiwa a tsakaninsu wajen gudanar da ayyukansu na ta'addanci, Saboda haka, a matsayinmu na kasashen nahiyar Afirka, dole ne mu dauki matakan da suka dace ta hanyar hadin gwiwa tare da hada kai wajen musayar bayanai, yin aiki tare, da kuma bin diddigin wadannan 'yan ta'adda a duk inda suke.

Kungiyar ISIL dake gudanar da ayyukanta a kasashen Muzambik da Uganda da kuma gabashin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo,ta yi barazana a shekarar da ta gabata cewa, za ta dauki mataki kan duk kasar da ta tura sojoji zuwa Mozambique domin yaki da su.
 
A cikin watan Yulin bana, sojojin Afirka ta Kudu da wasu kasashen yankin sun shiga birnin Cape Delgado (arewacin Mozambique) domin yakar kungiyar ISIL a wani bangare na rundunar sojan kasashen kudancin Afirka (SADC).
 
Tun da farko dai kungiyar al-Shabaab ta kai hare-haren ta'addanci da dama a Somaliya a matsayin ramuwar gayya ga shigar sojojin Kenya a cikin kasar domin yakar kungiyar.
 

4015846

 

 

 

 

captcha