Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Iran Saeed Khatibzadeh ya ce, kasarsa ba ta karbar izini daga kowa a duniya domin inganta ayyukanta na tsaro.
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran yayin da yake yin watsi da matsayin ma'aikatar harkokin wajen kasar Burtaniya na shiga tsakani kan karfin tsaron kasarsa ya ce: Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana aiki ne bisa tsarin dokokin kasa da kasa, daidai da bukatun tsaronta, inda ya ce furucin na Burtaniya shiga cikin harkokin cikin gida ne na Iran, tare da yin harshen damo a kan batutuwa na siyasa da suka shafi Iran da kuma wasu kasashen yankin.