IQNA

Ci gaba da gyaran tsoffin kwafin kur'anai a kasar Libiya

15:58 - April 05, 2022
Lambar Labari: 3487127
Tehran (IQNA) A daidai lokacin da watan Ramadan ya shigo, wasu gungun masu aikin sa kai ba dare ba rana domin gyara tsofaffin kur'anai da suka lalace suna gudanar da aiki a birnin Tripoli fadar mulkin kasar Libiya.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya nakalto daga  Farance 24 cewa, Khalid al-Darby daya daga cikin mashahuran masu gyaran kur'ani mai tsarki a kasar Libiya na daya daga cikin masu wannan aiki da ke zuwa wani taron bita a birnin Tripoli a kullum domin biyan bukatu masu yawa na kwastomomi a cikin watan Ramadan.

Al-Darby ya shaidawa kamfanin dilancin labaren AFP cewa, ana samun karuwar sayen sabbin kur'ani a bisa al'ada kafin watan Ramadan, amma a baya-bayan nan lamarin ya sauya a Libiya.

Ya kara da cewa: Sayen wannan littafi mai tsarki ya yi matukar wahala musamman ganin yadda gwamnati ta daina buga kur'ani a kasar Libiya.

Kasar da ke arewacin Afirka ta shafe fiye da shekaru goma tana fama da tashe-tashen hankula, kuma da yawa daga cikin cibiyoyinta sun durkushe, lamarin da ya yi mummunar illa ga kasar mai arzikin man fetur.

رونق کارگاه مرمت قرآن‌های قدیمی در پایتخت لیبی

Al-Darby yana cewa: "Kudin sayen kur'ani ya karu, don haka gyaran  tsoffin kur'ani ya zama wanda ba a taba ganin irinsa ba a kasar."

Idan aka kwatanta da farashin sabon kur’ani, wanda ya haura dalar Amurka 20, Al-Derby ya ce daloli kadan ne kawai zaa bayar don gyaran kur’ani. Amma kuma batun tsada ba ne kawai a cikin al'amarin, mutane da yawa suna kallon tsoffin kur’anai a  matsayi na musamman.

 

 

 

https://iqna.ir/fa/news/4046704

captcha