IQNA

20:08 - May 12, 2022
Lambar Labari: 3487283

Ana Gaba Da Yin Tir Da Isra’ila Kan Kisan ‘Yar Jarida Shireen Abu Akleh

Tehran (IQNA) Bangarori daban-daban a duniya na ci gaba da mayar da martani dangane da kisan da Isra’ila ta yi wa fitacciyar ‘yar jarida a Palestine Shireen Abu Akleh a jiya Laraba.

Ana Gaba Da Yin Tir Da Isra’ila Kan Kisan ‘Yar Jarida Shireen Abu Akleh

Kungiyar ‘yan jarida ta duniya ta fitar da bayanin yin Allawadai da kakkausar murya kan kisan Shireen, tare da dora alhakin hakan a kan gwamnatin Isra’ila, kamar yadda kungiyar ta bukaci da a gudanar da bincike kan lamarin, wanda zai kunshi bangarori na kasa da kasa.

Su ma a nasu bangaren Amurka da Tarayyar Turai da kuma Majalisar Dinkin Duniya, Kungiyar Hadin Kan Kasashen Larabawa, da kungiyoyin kare hakkin bil adama na kasa da kasa, duk sun bukaci da a gudanar da bincike na bangarori masu kansu kan wannan lamari.

A nata bangaren gwamnatin Falastinawa ta bayyana cewa, yanzu haka ta fara hada fayil-fayil kan wannan batu domin mika shi ga kotun hukunta manyan laifuka ta duniya, domin shigar da kara a kan Isra’ila, dangane da kisan Shireen Abu Akleh.

Kungiyoyin Hamas, Hizbullah, Jihad Islami, Ansarullah ta Yemen (Alhuthi) da kungiyoyin gwagwarmaya a Iraki, duk sun fitar da bayanai na yin Allawadai da kisan Shireen.

Sojojin yahudawan Isra’ila sun harbe Shireen Abu Akleh ne a safiyar jiya a lokacin da take daukar rahoto a wani samame da sojojin Isra’ila suka kai kan Falastinawa a yankin Jinin da ke gabar yammacin Kogin Jordan a Falastinu.

4056412

 

captcha