
Kamfanin dillancin labaran kur’ani na iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Barratha cewa, shugaban kwamitin kolin tsaro kuma gwamnan Karbala Nasif al-Khattabi ya jaddada cewa, za a dauki tsauraran matakai don tunkarar mutanen da suke da niyyar cin mutuncin birnin Karbala. An cire itatuwan kirsemiti da aka gani a titunan birnin na Karbala a daidai lokacin da ake gudanar da bukukuwan sabuwar shekara tare da kawar da wadannan bishiyun daga titunan birnin na Karbala.