Karbala (IQNA) Gwamnan Karbala ya sanar da cewa, za a dauki mataki mai tsanani ga mutanen da suke da niyyar cin mutuncin birnin da kuma sunan addini na Karbala, sannan ya ba da umarnin tattara bishiyar Kirsimeti a fadin lardin daga jiya Juma'a.

Kamfanin dillancin labaran kur’ani na iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Barratha cewa, shugaban kwamitin kolin tsaro kuma gwamnan Karbala Nasif al-Khattabi ya jaddada cewa, za a dauki tsauraran matakai don tunkarar mutanen da suke da niyyar cin mutuncin birnin Karbala. An cire itatuwan kirsemiti da aka gani a titunan birnin na Karbala a daidai lokacin da ake gudanar da bukukuwan sabuwar shekara tare da kawar da wadannan bishiyun daga titunan birnin na Karbala.