
Jaridar Alharam ta kasar Masar ta bayar da rahoton cewa, a cikin wani bayani da babbar cibiyar muslunci ta Azhar ta fitar ta bayyana cewa, Rufe masallacin da hana yin sallah a cikinsa laifi na kasa.
Bayanin na cibiyar AQzhar ya yi ishara ne da matakin da gwamnatin yahudawan sahyuniya suka dauka ne na rufe masallacin kudus a cikin wannan wata na Ramadan tare da hana dubban daruruwan musulmi yin salla a cikinsa.
Wannan shi ne karon farko da gwamnatin yahudawan sahyuniya ta dauki wannan mataki na hana yin duk wata salla a cikin masallacin Kudus, musamman a cikin watan da aka saba gudanar da salloli na tarawihi a kowace shekara.
Baya ga haka kuma ana gudanar da ibadar Itikafia cikin masallacin kudus a kowace shekara da musulmi suke yi, amma a shekarar bana Isra'ila ta hana, domin kuwa ta kulle masallacin kuma ta killace shi da jami'an tsaro.
4340908