
A cewar jaridar France 24, Hadaddiyar Daular Larabawa ta Kori dubban 'yan Shi'a 'yan Pakistan daga kasar.
Wannan matakin ba wai kawai ya kori wadannan mutane ba ne, har ma ya daskarar da dukkan kadarorinsu, asusun banki da dukiyar da suka samu da wahala, wanda hakan ya mayar da su Pakistan hannu wofi.
Wannan matakin ya zo ne a daidai lokacin da ake ci gaba da samun takun saka tsakanin Abu Dhabi da Islamabad.
"Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ta Kori 'yan Shi'a 'yan Pakistan 15,000 wadanda suka mayar da kasar Gulf gida tsawon shekaru ashirin da suka gabata," in ji Surbhi Gupta, editan Kudu maso Gabashin Asiya a mujallar New Lines.
4350100