IQNA

20:25 - August 01, 2014
Lambar Labari: 1434785

Cibiyoyin Addini A Najeriya Na Allawadai Da Kisan Masu Jerin Gwanon Ranar Quds

Bangaren kasa da kasa, cibiyoyin addinin muslunci da dama sun yi Allawadai da kisan gllar da sojojin Najeriya suka yi wa musulmi masu gudanar da zanga-zangar ranar Quds domin nuna goyon baya ga al'ummar palastine.

Kamfanin dillancin labaran Iqna ya habarta cewa, kungiyoyin addini da dama a Najeriya sun  yi Allawadai da kisan gllar da sojojin kasar  suka yi wa musulmi masu gudanar da zanga-zangar ranar Quds domin nuna goyon baya  ga al'ummar palastine a birnin Zaria.

A nasa bangaren Jagoran harkar Musulunci a Nigeriya Sheikh Yakub Ibrahim El-Zakzaki ya bayyana cewar babu wani mutum da ke dauke da makami a lokacin da sojojin gwamnatin Nigeriya sun farma ‘yan uwa da suke gudanar da zanga-zangar ranar Qudus ta duniya, kuma a tsawon tarihin harkar Musulunci a kasar babu wani lokaci da ‘yan uwa suka taba sabar makami domin kare kansu.

A dan takaitacciyar zantawar da ya yi da manema labarai ta hanyar wayar tarho a yau Asabar; Jagoran harkar Musulunci a Nigeriya Sheikh Yakub Ibrahim El-Zakzaki ya bayyana cewa; babu wani dan uwa da ke dauke da makami a lokacin da sojojin gwamnatin Nigeriya suka farma masu a yayin gudanar da zanga-zangar ranar Qudus ta duniya a jiya Juma’a, kuma duniya ta isa shaida kan cewa; a tsawon tarihin harkar Musulunci a Nigeriya babu wani lokaci da ‘yan uwa suka taba daukan makami, don haka zamu ci gaba da zaman sauraron irin karyaryakin da zasu dinga furtawa a kanmu.

Sheikh Zakzaki ya kara da cewar yau tsawon shekaru kimanin 40 muna gudanar da irin wannan zanga-zanga, kuma an gudanar da zanga-zangar ranar Qudus ta duniya a sassa daban daban na Nigeriya kuma babu abin da ya faru, sai a garin Zariya da sojojin gwamnati suka bude mana wuta ba gaira babu dalili alhali a tsakaninmu akwai mata da kananan yara da kuma tsofaffi.

A jiya Juma’a ce dai sojojin gwamnatin Nigeriya suka bude wuta kan taron jama’a da ke gudanar da zanga-zangar ranar Qudus ta duniya a garin Zariya lamarin da ya yi sanadiyar shahadar mutane akalla 31 cikin har da ‘ya’yayen jagoran harkar Musulunci a kasar guda uku Ahmad, Hameed da Mahmud tare da jikkata wasu masu yawa na daban.

1434196

Abubuwan Da Ya Shafa: quds
captcha