IQNA

An Girmama Wadanda Suka Nuna Kwazo A Gasar Kur'ani Ta Talabijin A Mauritania

12:50 - October 23, 2014
Lambar Labari: 1463120
Bangaren kasa da kasa, an girmama wadanda suka kwazo a gasar karatun kur'ani mai tsarki wadda aka gudanar kai tsaye ta gidajen talabijin na kasar Mauritanita da ake kira gasar kur'ani ta talabijin.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya ahbarat cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo cewa, an gudanar da taron girmama wadanda suka kwazo a gasar karatun kur'ani mai tsarki wadda aka gudanar kai tsaye ta gidajen talabijin na kasar Mauritanita da ake kira gasar kur'ani ta talabijin a kasar, wadda aka saba yi a cikin 'yan shekaru da suka gabata.

Bayanin ya ci gaba da cewa shugaban hukumar kula da ayyukan kur'ani a ma'akatar kula da harkokin addinin muslunci a kasar Sidi Muhammad wold Sheikh shi ne ya jagoranci gudanar da wannan gasa, wadda ta kasance a sahun gaba a cikin ayyukan da ake gudanarwa a halin yanzu a bangaren da ya shafi kur'ani mai tsarki a kasar ta Mauritaniya.

Daga cikin bangarorin da suka gudanar da wannan gasa kuwa hard a dattijai wadanda suka kasance a sahun gaba  acikin mahardata na kasar, wadanda kuma sun samu kyutuka na girmama sakamakon kwazon da suka nuna a wanann gasa, da kuma irin hidimar da suka yi kur'ani ami tsarki na tsawon lokaci a rayuwarsu, kamar dai yadda majiyoyin hukumar suka tabbatar da hakan.

Babban dakaraktan hukumar radiyo da talabijin na kasar Mauritaniya ya kasancea  wurin a lokacin bayan da kyuatukan, inda ya ya yaba matuka da irin gagarumin ci gaban da wannan gasa ta samu a shekarar bana.

1462777

Abubuwan Da Ya Shafa: mauritania
captcha