Kamfanin dillancin labaran Iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na jaridar Yaum Sabi cewa masana sun gabatar da sabuwar taswira ta sake gina masallacin jami’ar Azhar babbar cibiyar addinin mulsunci mafi girma a kasar wadda ke babban birnin Kasar da ake ci gaba da yin wannan aiki babu tsayawa.
A nasa bangare kuwa babban malamin Azhar na kasar Masar ya nuna damuwarsa dangane da samuwar masu akidar kafirta musulmi a wasu kasashen larabawa da na musulmi. Kanfanin dillancin labarai na kasar Iran ya habarta cewa a yau assabar jami'ar Al'azhar ta kasar Masar ya bayyana a tashar telbijin ta kasar inda ya bayyana damuwarsa dangane da samuwar akidar kafirta musulmi a wasu kasashen larabawa da na musulmi
Inda yace masu wannan akida sun eke badda matasa musulmi kuma sun fi makiya musulinci hadari saboda sune suka bayar da fatuwa na kashe Al'ummar musulmi da sunan musulinci kamar yadda yake faruwa a kasashen Siriya,Iraki, Lobnon da kuma abinda yake faruwa yanzu haka a kasar Masar.
Malamin Azhar yace masu irin wannan akida sune suka bada fatawar halarta jinin jami'an 'yan sanda da na Sojoji a kasar ta Masar kuma suke baiwa Al'ummar kasar umarni fito na fito da hukumomi a kasar.
Kafin wannan bayanai, an kara fadada kai hare hare kan dakarun tsaron kasar Masar daga kungiyoyin masu dauke da makamai tare da wasu mayaka masu alaka da kunigyar Ansaru baitul mukkadas a yankin tsibirin Sina bayan samun umarni daga ahiri shugaban kungiyar kaida na kasar ta Masar.
1470889