Kamfanin dilalncin labaran Iqna ya habarat cewa, ya naalto daga safin sadarwa na yanar gizo na Sautul Iraq cewa, yan ta'addan kungiyar ISIL na shirin rusa masallatai masu tarihi a garin Mausil, bayan sun yanka limamin babban masallacin birnin Mausil a arewacin kasar Iraki, bayan da yaki ya mika musu masallacin, da kuma kin bayar da fatawar korar kiristoci daga birnin.
Wani daya daga cikin shugabannin kabilun larabawa 'yan sunna a garin Mausil Sheikh barham ya bayyana wa tashar talabijin ta Iraqi a daren jiya cewa, 'yan ta'addan sun bukaci malamin da ya mika musu masallacin kuma ya bayar da fatawar haramcin barin kiristoci a cikin garin na Mausil, inda ya sheda musu cewa ba zai yi hakan ba, a nan take suka yanka shi.
A nasu bangaren sojojin kasar Iraki suna ci gaba da nausawa a cikin yankunan da 'yan ta'addan suka kwace iko da su, inda suke ci gaba da fatattakarsu, domin dawo da doka da oda a yankunan, da kuma dawo da dubban daruruwan mutanen da 'yan ta'addan suka kora daga yankunansu.
Wannan na daga cikin ayyukan da yan ta'addan suke aiwatrwa a kasar tare da yin kisan gilla a kan fararen hula mata da kanann yara da suke cikin wadannan yankuna a na arewacin kasar.
2620500