
Kamfanin dillancin labaran Iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na jaridar Al-shuruq cewa, kawancen jam’iyyun da ke kan karagar mulkin Jamhuriyar Nijar ya bukaci al’ummar kasar baki daya da su gudanar da zanga-zangar nuna goyon baya ga gwamnatin kasar wadda ta kuduri aniyyar fada da mayakan Boko Haram da suka soma kai wa kasar hare-hare.
Jam’iyyun siyasar sun bukaci a gudanar da wannan zanga-zanga a ranar 17 ga wannan wata na Fabarairu a duk fadin kasar.
Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da shugaban kasar Mahamadou Issifou ya bukaci al’ummar kasar da su mara wa sojoji da kuma sauran jami’an tsaron kasar baya a kokarin da suke na kare iyakokin kasar daga barazanar wannan kungiya.
A cikin yan lokutan nan mayakan na Boko Haram sun kaddamar da hare-hare a cikin yankuna na kasar ta Nijar, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama.