IQNA

‘Yan Jarida Daga Kasashe 17 Ne Za Su Halarci Taron 14 Ga Khordad

23:47 - June 01, 2015
Lambar Labari: 3310279
Bangaren kasa da kasa, a daidai lokacin da ake shirin gudanar da taron cika shekaru 26 na rasuwar Imam Kohmeini (RA) yan jarida 80 ne tare da masu daukar hotuna daga kasashen ketare za su halarci wannan taron.


Kamfanin dillancin labaran Iqna ya habarta cewa, Mohammad Mansur Koshesh babban jami’I mai kula da harkokin yada labarai na ma’aikatar kula da harkokin al’adu na jamhuriyar muslunci ya bayyana cewa, wadannan yan jarida da masu daukar hotuna suna aiki ne a karkashin kafofin yada labarai guda 26 na kasashen ketare, kuma daga kasashe 17, kuma duk za su halarci taron na rasuwar Imam Khomeini (RA) domin daukar labarai da bayanai kan taron baki daya.

Ya kara da cewa kasashen su ne Japan, England, Turkiya, Amurka, UAE, Lebanon, Iraki, Qatar, Kuwait, Afghanistan, Colombia, China, Luxumburg, Italia, Sweeden, Jamus, da kuma Switzerland su ne kasashe 17 da yan jarida za su halarci taron na 14 ga Khordad a kasar Iran.

3310029

Abubuwan Da Ya Shafa: iran
captcha