IQNA

Daesh ta sare Kan Limamin Masallacin Al-salihin Na Birnin mausil

22:02 - July 24, 2015
Lambar Labari: 3332512
Bangaren kasa da kasa, yan ta’addan daesh sun sare kan daya daga cikin malaman addinin muslunci kuma limamin masallacin Alsalihin da ke yammacin birnin Mausil na kasar Irakia jiya.


Kamfanin dillancin labaran Iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Saumariyyah news cewa, a jiya  ne yan ta’addan daesh suka sare kan Sheikh Nakshabandi daya daga cikin malaman addinin muslunci kuma limamin masallacin Alsalihin da ke yammacin birnin Mausil da ke karkashin ikonsu.

Wani wanda ya bukaci da a sakaya sunansa ya bayyana cewa, yan ta’addan sun kashe wannan malami ne bisa hujjar cewa ba ya bin irin koyarwar da suka yarda da ita, kuma suka bayar da umarni da a yi aiki da ita a yankin, a kan hakan haka hukuncin kisa ya ha kansa.

A ranar Litinin da ta gabata ce yan ta’addan suka harbe daya daga cikin malaman yankin Shekh Najmuddin Kan’an Aljaburi kuma limamin masallacin Alhumaid, ta hanyar yin amfani da harsashen bindiga a kansa.

Yan ta’addan sun kash malamai da dama a Masil tun bayan kwace iko da yankin a cikin watan Yunin shekara ta 2014, tare da taimakon wasu daga cikin kasashen da ke makwabtaka da kasar ta Iraki.

Ya zuwa yanzu dai yan ta’addan sun kashe malamai da kuma al’umar gari masu tarin yawa bisa hujjoji daban-daban, musamman ma dais aba umarininsu da kuma kallonsu a matsayin wadanda ba kan sahihin tafarki suke ba, domin kuwa suna kallon kowa a matsayin kafiri sai dai wanda ya shiga cikinsu.

3332435

Abubuwan Da Ya Shafa: iraki
captcha