IQNA

Abin Da Ya Faru Mai Sosa Zuciya Ne/A Shiye Muke Mu Taimaka Ma Wadanda Suka Samu Raunuka

21:49 - September 12, 2015
Lambar Labari: 3361733
Bangaren siyasa, Dr. Rauhani a cikin wani sako da ya fitar dangane da abin da ya faru a haramin Makka ya bayyana cewa ko shakk abu ne mai sosa rai matuka kuma a shirye suke su taimaka ma wadanda suka samu rauni.


Kamfanin dillancin labaran Iqna ya habarat cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na ofishin shugaban kasa cewa, matain sakon shugaban kasa kamar haka:

Da Sunan Allah mai rahma Mai Jin Kai

(Farko daki da aka saka ma mutane shi ne wanda yake a Makka mai albarka kuma shiya ga talikai)

Rasa rayukan da alhazai suka yi a kasa mai tsarki da suka hada har da alhazai Iraniyawa, hakika wannan abu ne mai sosa zuciya da saka damuwa da bakin ciki matuka.

Wanann lamari ya faru ne a cikin kwanaki da ake gudanar da aikin hajji a daki mai alfarma tare da halartarv musulmi dag akoina cikin fadin duniya, wanda hakan abin bakin ciki ne, kuma muna isar da sakon taya bakin ciki ga wadanda abin ya shafa baki daya.

Shugaban kasar Iran ya aike da sakon ta'aziyya ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu a cikin masallacin Harami mai tsarki a Makka, tare yin addu'ar Allah ya jikansu da rahama ya gafarta musu, haka nan kuma ya bayyana cewa Iran a  shirye take ta karbi dukkanin wadanda suka samu raunuka domin yi musu magani.

Hassan Rauhani shugaban kasar Iran

3361608

Abubuwan Da Ya Shafa: iran
captcha