IQNA

Hare-Hare A Masallatai Biyu A najeriya Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutane 55

21:31 - October 25, 2015
Lambar Labari: 3393614
Bangaren kasa da kasa, wasu hare-haren da aka kai kan wasu masallatai a yankunan arewa maso gabacin Najeriya ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 55.


Kamfanin dillanicn labaran Iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na tashar Ruusia Today cewa, hare-haren da aka kai a yankunan arewa maso gabacin Najeriya ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 55. Tare da jikkatar wasu fie da 100.

Hukumomi a jihar Adamawa da ke arewa maso gabashin Najeriya sun ce mutane 27 ne suka mutu a harin bam din da aka kai a birnin Yola, kakakin gwamnatin jihar ya shaida cewa mutane 96 ne suka samu raunuka.

Wadansu da suka shaida lamarin sun ce an tayar da bam din ne a Masallacin Jambutu da ke Jimeta a dai-dai lokacin da ake tayar da Sallar Juma'a.

A can Maiduguri babban birnin Jihar Borno mutane na ci gaba da zaman jimami bayan wasu hare-haren da suka yi sanadiyyar mutuwar mutane akalla 28 tare da jikatar wasu da dama.

3393040

Abubuwan Da Ya Shafa: najeriya
captcha