
Kamfanin dillancin labaran Saba ya ce,
ya nakalto daga Aiman Abdulkadir babban darakatan ma’aikatar kula da harkokin
addini cewa, Saudiyya ta rusa masallati 49 kai tsaye a cikin birnin, wasu 87
kuma a wasu sassa na lardin.
Abdulkadir ya ci gaba da cewa yanzu
haka akwai masallatai 19 da ta rusa a yankin Sanhan da Bani Bahlul, sai kuma
wasu 13 a garin Hada da kuma 5 a Bilad Rus, 3 a Bani Matr, 3 kuma a Niham, sai
kuma 4 a Hilam da khema Dakhilyah, da kuma Bani Hashish da Hujanah.
Ya kara da cewa kashi 80% na
dukaknin masallatan da Saudiyya ta rusa a kasar Yemen suna da alaka ne da
tarihi, wati masallatai ne wadanda aka gina daruruwan shekaru da suka gabata da
ake lissafa su a cikin wuraren tarihi na kasar.
Abdulkadir y ace Saudiyya tare da
kawayenta da suka hada da larabawa da turawa, su ne suke da hannu kai
tsayea dukkanin abin da yake faruwa na
kisan fararen hula da rusa kasar Yemen.