IQNA

Zanga-Zangar Kin Muslunci A Kasashe 14 Na Nahiyar Turai

23:00 - January 26, 2016
Lambar Labari: 3480081
Bangaren kasa da kasa, kungiyoyin masu adawa da addinin musulunci a cikin nahiyar turai da suka hada da PEGIDA za su gudanar da gangami a kasashe 14 na nahiyar turai.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa ya naklato daga shafin sadarwa na yanar gizo cewam kungiyar ta PEGIDA za ta jagoranci gudanar da zanga-zanga a kasashe 14 na turai a cikin mako mai zuwa, domin nuna rashin amincewa da a bin da suke kira musuluntar da nahiyar turai, kasashen sun hada Chek, Jamus, Istuania, Solvakia da Switzerland.

Daya daga cikin wadanda suka shirya wannan taro ya bayyana cewa za su gudanar da nasua  babban birnin kasar Chek, inda za su taru domin nuna rashin yardarsu da kokarin mayar da nahiyar turai ta musulmi.

Ya ce dukkanin mutanen nahiyar turai manufarsu guda ce ta rashin amincewa da musuluntar da wannan nahiya ta su.

Kungiyar PEGIDA dai an kafa ne a cikin shekara ta 2014 a kasar Jamus, domin nuna rashin amincewa da yaduwar addinin muslunci a kasar ta Jamus, daga bisani kuma akidar kungiyar ta ci gaba da bazuwa zuwa wasu kasashen nahiyar turai.

Dangane da batun karbar yan gudun hijira da gwamnatin Jamus ta ce ta yi da suka hada mafi yawansu musulmi, kungiyar ta kara tsananata ayyukan na kiyaye da addini muslunci, kamar yadda ta yi taro a kan hakan a birnin Colen na kasar Jamus.

3470438

captcha