IQNA

Bangaladesh Ta Jaddada Matsayinta Na Ci Gaba Da Rufe Tashar Zakir Naik

22:08 - July 11, 2016
2
Lambar Labari: 3480600
Bangaren kasa da kasa, Mahukunta a kasar Bangaladesh sun jaddada matsayinsu na ci gaba da rufe tashar malamin salafiyyah Zakir Naik, inda suka ce wannan tasha tana yada tsatsauran ra'ayi wanda sanadiyyar hakan ne aka kai harin ta'addanci a kasar a makon da ya gabata.
Kamfanin dillanicn labaran iqna ya habarta cewa ya nakalto daga Jaridar Quds Al-arabi mallakin gwamnatin atar da ake bugawa abirnin landa ta bayar da rahoton cewa, mahukuntan kasar ta Bangaladesh sun ce Zakir Naik wanda malamin salafiyyah ne, yana yada tsatsauran ra'ayi, kuma dukkanin matasa biyar da suka kaddamar da harin ta'addanci tare da kashe mutane 22 a makon da ya gabata, sun tasirantu ne da kalamansa da ake watsawa ta hanyar wannan tasha, a kan haka an rufe tashar tare da haramta masa shiga kasar.

Assad Zaman Khan ministan harkokin cikin gidan kasar Bangaladesh ya fadi jiya a zantawarsa da manema labarai cewa, jami'an tsaron kasar suna cikakken bayanan sirri kan cewa dukkanin masu alaka da kungiyoyin 'yan ta'adda a kasar mutanensa ne, kuma yanzu suna bincike kan kasashen da suke daukar nauyinsa da ba shi kudade wajen yada akidar salafiyanci da wahabiyanci da ke haifar da tsatsauran ra'ayi wanda ke kai matasa shiga kungiyoyin 'yan ta'adda.

Wasu daga cikin kasashen turai da Asia sun kafa dokar hana Zakir Naik shiga cikin kasashensu, bisa abi da suka kira kauce wa yada tsatsauran ra'ayi a tsakanin matasa musulmi.

3514076

Wanda Aka Watsa: 2
Ana Cikin Dubawa: 0
Ba A Iya Watsa Shi: 0
Sadiq yusuf
0
0
Gaskiya hakan yayi dai dai dan wahabiyanci bala'ine a duniyar musulmai
muhd lawan isyaku
0
0
to Allah Yayi manatsari da kaucewa gaskiya
captcha