IQNA

Gungun matasan 14 ga Fabrairu

Ana Ci Gaba Da Yin Allawadai Da Kama Manyan Malamai A Bahrain

23:47 - August 09, 2016
Lambar Labari: 3480693
Bangaren kasa da kasa, Gungun matasan 14 ga Fabrairu ya yi Allawadai da kakkausar urya dangane da ci gaba da kame manyan malaman addinin muslunci na kasar Bahrain da masarautar mulkin kama karya ta kasar ke yi.
Kamfanin dilalncin labaran kur'ani na Iqna ya habarta cewa, Shafin jaridar Manama Post ya bayar da rahoton cewa, a yau gungun matasan 14 ga Fabrairu ya fitar da wani bayani, wanda a cikinsa ya bayyana ci gaba da kame mayna malamai masu tasiri a kasar da masarautar kama karya ke yi, ya nuna irin yanayin da sarakunan kasar ke ciki na kaduwa da kuam tsorata da tasirin malaman.

Bayanin ya ce masarautar Bahrain tana tafka babban kure, domin kuwa malaman da take kamawa su ne suke tausasa al'ummar kasar daga yin duk wani gagarumin bore da zai kifar da masarautar baki daya, kuma ci gaba da yin hakan zai gaggauta kawo karshen mulkin masarautar kama karya da turawan mulkin mallaka suka kafa a kasar.

A baya-bayan nan masarautar Bahrain ta kame manyan malamai da suka nuna rashin amincewarsu da matakin da ta dauka na janye izinin zam dan kasa daga kan babban malamin addini na kasar Sheikh Isa Kasim, malamin da fiye da rabin al'ummar kasar ke kallonsa a matsayin shugabansu an addini.

Daga cikin manyan malaman da aka kame a cikin makon nan har da Sayyid majid Mash'al, shugaban majalisar malaman kasar, da kuam sheikh Ali Muhli, da sheikh Fadil Zaki, da kuam Sayyid Muhsin Al-guraifi, dan Allamah Al-guraifi.

3521338

captcha