IQNA

An Yi Gargadi Dangane Da Raba wani Kur’ani Mai Kura-Kurai Bugun Azahar

23:44 - August 18, 2016
Lambar Labari: 3480723
Bangaren kasa da kasa, babban malami mai bayar da fatawa a Palastine ya yi gargadi danagane da yada wani kur’ani da yake dauke da kure.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa ya nakalto daga kamfanin dillancin labaran Palastine cewa, Sheikh Muhammad Hussain babban malamin yankin kuma shugaban majalisar shawara ta malaman Quds ya bayyana cewa, kwafin kur’anin da cibiyar Taufikiyya ta buga yana dauke da kure a cikin shafukan 484 zuwa 517 a cikinsa.

Ya kara da cewa wannan cibiyar ta buga kur’anin ne tare da samun izinin daga cibiyar Azahar, takardar iznin tana dauke da lamba 25 a ranar 19/4/2011, alhali akwai manyan kura-kurai a cikin bugun wanda jami’ar Azahar ba ta yi la’akari da shi ba.

Malamin ya ce bai halasta a yi amfani da wannan kwafin kur’ani ba, kuma ya umarci dukkanin usulmin Palastine da su tatatra duk wani kwafi da ke a hannunsu su mika ga ofishin kula da harkokin shari’a, domin yin dubi kana bin da za a yin a gyara.

3523729

Abubuwan Da Ya Shafa: iqna palastine
captcha