Kamfanin dillancin labaran kur’ani na iqna ya
habarta cewa, ya nakalto daga Shafin
yada labarai na First Post ya habarta cewa, shugabar gwamnatin kasar Jamus
Angela Markel ta bayyana matakin da wasu daga cikin kasashen turai suke dauka
kan musulmi 'yan gudun hijira da cewa ya yi hannun riga da 'yan adamtaka.
Markel ta ce tana fatan kasashen kungiyar tarayyar turai da suka daukin matakin hana 'yan gudun hijira musulmi shiga kasashen za su sake yin nazari kan wannan mataki, domin kuwa hakan ya sabawa manufofin kafa kungiyar.
Tun bayan da 'yan gudun hijira na kasashen larabawa musamman an na Syria suka fara shiga nahiyar turai, wasu daga cikin kasashen suka sanar da rufe iyakokinsu, musamman ga musulmi daga cikinsu.