Bayanin ya ce wannan mataki zai hada da rufe tashoshinsa na talabijin, da kuma makarantu, haka nan kuma za a gabatar da tuhuma a kansa kan saka matasa a cikin kungiyoyi na 'yan ta'adda, domin kuwa a cewar ma'aikatar harkokin cikin gidan kasar ta India, dukkanin matasan kasar ad suka shiga cikin kungiyoyin 'yan ta'adda da ke yaki a Syria da Iraki almajiransa ne.
A nata bangaren gwamnatin kasar Bangaladash ta ce wadanda suka kai hare-haren ta'addanci a kasar a kwanakin baya suna daga cikin mabiyansa, wanda hakan ne yasa aka haramta masa shiga kasar.