Hilal Ahmad daya ne daga cikin mambobin kwamitin masallacin ya bayyana cewa, ya ga mutanen biyu a lokacin da suke jefa naman alade kan masallacin a lokacin da ake salla, da farko ya yi zaton cewa ‘yan sanda ne, amma sai ya gas hi ma suna jefa masa naman alade, a lokacin sai ya fahim ci cewa masu tsokana ne.
Ya kara da cewa wannan dai shi ne karon farko da wani abu mai kama da haka a farua cikin shekaru takwas a jere da ya kwashe yana zuwa wannan masallaci yana gudanar da ibada.
Bayan yan mintuna da faruwar hakan, jami’an ‘yan sanda sun isa wurin tare da daukar matakan tsaro domin tabbatar da cewa sun bayar da kariya ga musulmi da suke salla a cikin masallacin.
Addinin mulsunci dai yana a matsayin addini na biyu mafi girma a kasar Birtaniya, inda yanzu haka akwai masallatai kimanin 600 da makarantun addnin muslunci guda 60 da aka gina a kasar.