Ali Shah daya daga cikin mahalarta wannan gangami da tattaki ya sheda ma manema labarai cewa, sun fito domin su nana damuwarsu da alhininsu dangane da abin da ya samu jikan manzon Allah (SAW) Imam Hussain (AS).
Ya ce wannan lamarti yana da matukar muhimmanci a gare su, domin hakan yana a matsayin taya manzon manzon Allah da iyalan gidansa bakin cikin abin da ya faru da su ne na zalunci da kisan gillar da aka yi kansu.
‘Yan sandan gwamnatin Birtaniya sun kasance tare da masu tattakin, domin ba su kariya, da kuma tabbatar da cewa wasu ba su kawo musu matsala ko rashin tsari a tattakin nasu ba.